✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi jana’izar Bello Maitama a Kano

An birne shi a makabartar Tarauni da ke Kano

An gudanar da jana’izar tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida na Najeriya kuma Sardaunan Dutse, Alhaji Bello Maitama Yusuf, a Fadar Sarkin Kano da yammacin Juma’a.

Marigayin dai ya rasu ne yana da shekara 76 a duniya, bayan gajeruwar jinya.

Ya rasu ya bar mata biyu da ƴaƴa 10; maza biyar, mata biyar.

Marigayin dai ƙwararran lauya ne wanda ya yi Minista a jamhuriya ta biyu kuma ya zama Sanata a jamhuriya ta huɗu.

An birne shi ne a makabatar Tarauni da ke birnin Kano kamar yadda Addinin Musulunci ya tanadar.

Ga wasu daga cikin hotunan jana’izar tasa: