✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi garkuwa da mai shekara 70 da wasu a Kogi

Bayan garkuwa da shi 'yan bindigar sun bukaci miliyan N50 kudin fansa

Ana zargin ’yan bindiga a kan hanyar Okene da yin garkuwa da wani mutum mai suna Mista Mike Oguguo Ndu daga Anambra tare da wasu matafiya.

Mista Ndu, wanda tsohon dan jarida ne ya hau motar haya ne domin ziyartar matarsa da ba ta da lafiga a Abuja.

Motar ta baro Onitsha zuwa Abuja ne a ranar Litinin da misalin karfe 7:20 na safe.

Tun bayar tasowarsa yake waya da iyalansa, amma misalin karfe 3 na yamma aka daina samunsa a waya.

Sai a ranar Talata ne aka kira dan uwansa Joseph Ndu, aka bukaci Naira miliyan 50 kudin fansa.

Bayan faruwar lamarin iyalansa sun je kamfanin motocin WAZOBIA da ke Gwagwalada a Abuja, inda Manajan kamfanin ya ce za a taimaka musu da bayanan da suke da shi game da batan mahaifin nasu.

Mike Ndu mai shekara 70 yana fama da matsanancin ciwon suga da hawan jini, yanayin da ke iya ta’azzara a hannun masu garkuwar.

Kafin Mista Ndu ya yi ritaya, ya yi aiki da kamfanin jarida Monitor da mujallar Enterprise da ke Oyo; gidan rediyon Madonna FM da ke Okija sai kuma jaridar The Nation a Onitsha.