An tura tubabben Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II zuwa zaman hijira a Jihar Nasarawa.
Jaridar Intanet ta Daily Sun ce ta bayyana haka, inda ta ce wasu majiyoyin Majalisar Masarautar Kano sun shaida mata cewa an fice da tsohon Sarkin daga fadar, kuma wadansu jami’an gwamnati da jami’an tsaro ne suka yi masa rakiya zuwa filin jirgin sama a hanyarsa ta zuwa Jihar Nasarawa.
A safiyar yau ce Gwamnatin Jihar Kano a karkashin Gwamna Abdullahi Ganduje ta tube tsohon Sarkin.