✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An rage wa ma’aikatan Kano lokutan aiki albarkacin watan Ramadana

An buƙaci ma’aikata su ribaci matakin domin bauta wa mahaliccinsu da yi wa jihar da kasa addu’a.

Gwamnatin Kano karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta rage wa ma’aikatanta lokutan gudanar da aiki a watan Ramadan mai kamawa.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai ɗauke da a hannun Sakataren Ofishin Shugaban Ma’aikata na jihar, Umar Muhammad Jalo.

Cikin sanarwar dai, a ranakun Litinin zuwa Alhamis ma’aikatan za su fara aiki ne daga karfe 8:00 na safe zuwa 3:00 na yamma, yayin da za a ci gaba da aiki yadda aka saba a ranakun Juma’a.

Sanarwar ta kuma ce matakin ya biyo bayan yunkurin gwamnatin na bai wa ma’aikatan damar bautawa mahaliccinsu, da kuma yi wa Jihar Kano da ma kasa baki ɗaya addu’ar samun zaman lafiya da ci gaba.