✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An sako daliban da aka yi garkuwa da su a Ekiti

An sako daliban da malaman nasu ne kimanin mako guda bayan an yi garkuwa da su

Dalibai tara da malamansu da aka yi garkuwa da su a Jihar Ekiti sun kubuta daga hannun ’yan bindiga.

Da misalin karfe 2 na dare, kafin wayewar garin yau Lahadi ne masu garkuwa da su suka sako su.

Hukumomi a jihar sun tabbatar da sako daliban su tara tare da malamansu.

An sako daliban da malaman nasu ne kimanin mako guda bayan an yi garkuwa da su a makarantar Apostolic Faith Group of Schools da ke yankin Emure-Ekiti.

Kawo yanzu dai babu bayanin ko an biya kudin fansa.

An yi garkuwa da su ne a makarantar Apostolic Faith Group of Schools da ke yankin Emure-Ekiti.