✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kwaso ’yan Najeriya 151 da ke gararamba a Libya

Wannan shi ne ayarin farko da aka kwaso a bana

Gwamnatin Tarayya tare da hadin gwiwar Hukumar Kula da ’Yan Ci-rani ta Duniya (IOM)  a ranar Talata sun kwaso wasu ’yan Najeriya kimanin 151 da ke gararamba a birnin Benghazi na kasar Libya.

Jami’in ofishin jakadancin Najeriya da ke Libya, Kabiru Musa ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwar da ya ba Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a Abuja ranar Talata.

Ya ce daga cikin mutanen, 71 mata ne, 54 maza, sai kananan yara 14 da jarirai 13, kuma tuni suka sauka a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas da misalin karfe 8:00 na dare.

Ya ce ko a shakara ta 2022, sai da IOM da hadin gwiwar Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya suka sami nasarar kwaso ’yan Najeriya kimanin 4,000, wadanda ke zaune a kasar ba bisa ka’ida ba.

Ya ce mutanen da aka kwaso na ranar Talata su ne rukunin farko a bana, kuma suna sa ran kwaso wasu da dama a nan gaba kadan.

Kabiru ya kuma ce ranar Laraba za a kara kwaso wasu karin ’yan najeriyar daga birnin Tripoli, yayin da ake sa ran sake kwaso wasu ranar 3 ga watan Afrilu daga birnin misrata, duka a Libyan. (NAN)