✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kori dalibin da ya lakada wa malamarsa duka a Jami’ar Ilorin

Ya yi mata jina-jina har ta kai ga an yi gaggawar mika ta asibiti.

Jami’ar Ilorin ta kori dabin nan da ya lakada wa malamarsa duka, Salaudeen Waliu Aanuoluwa na Sashen nazarin kananan halittu wato Microbiology.

Sanarwar da Darektan Harkokin Makarantar, Mista Kunle Akogun ya fitar, ta ce an yanke wannan hukuncin ne a gaban Kwamitin Ladabtar da Dalibai wanda Salaudeen ya tsaya gabansa a ranar Litinin.

BBC ya ruwaito cewa, Kwamitin ya bai wa dalibin kwanaki 48 domin ya daukaka kara gaban Kwamitin Shugaban Jami’ar.

“Tuni aka mika wa ’yan sanda Salaudeen domin daukar matakin da ya dace a kan shi,” a cewar sanarwar.

“Bayan amsa laifin da ya yi na rashin daa, Shugaban Jami’ar ya ba da umarnin a kori Salaudeen daga wannan jami’a.

Sai dai sanarwar ba ta yi karin haske ba a kan hujjar da bayar game da dukan malamar da ya yi, ko kuma wata hujja da ya bayyana domin kare kansa.

Ana iya tuna cewa Aminiya ta ruwaito cewa, dalibin na aji hudu ya lakada wa wata malamarsa dukan kawo-wuka daga ta ki ba shi taimakon da ya nema.

Dalibin da aka bayyana inkiyarsa a a matsayin Captain Walz, bai yi kwas din da ya wajaba dalibai su yi ba na samun horo da sanin makamar aiki da ake tura dalibai a shekarar gab da ta karshe ta karatunsu ba wato SIWES, (Students Industrial Work Experience Scheme).

Dalibin ya lakada wa Malamar mai suna Mrs Zakaria dukan tsiya a ranar Alhamis, wadda rahotanni suka ce a karkashin kulawarta ne zai yi bincike da nazari da daliban ajin karshen ke gudanarwa gabanin kammala karatu a jami’a wato Project.

Bayanai sun ce, dalibin ya kai wa malamar ziyara har ofishinta domin neman taimako la’akari da kwas din sanin makamar aiki (SIWES) da bai yi ba.

Sai dai yayin da malamar ta hau kujerar naki da rashin bai wa dalibin hadin kai kan bukatar da ya zo mata da ita, a nan ne ya hau dokin zuciya inda ya yi mata jina-jina har ta kai ga an yi gaggawar mika ta asibiti.

Darektan Kula da Harkokin Gudanarwa na jami’ar, Mista Kunle Akogun, ya tabbatar wa da Aminiya hakan a wata tattaunawa ta wayar tarho da ya yi da wakilinmu a ranar Asabar.

“Eh tabbas wannan abun takaici ya faru amma a halin yanzu malamar ta farfado kuma tana samun kulawa a asibiti.

“Shugaban Jami’ar, Farfesa Abdulkareem Age ya kai mata ziyara tare da wasu manyan makarrabai da wasu ma’aikatan jami’ar.

“Sun bayyana lamarin a matsayin abun takaici tare da bayar da tabbacin cewa za a duk wata mai yiwuwa wajen bi mata hakkinta kamar yadda shari’a ta tanada.

“Shugaban jami’ar ya kuma bayar da umarnin a yi wa malamar kyakkyawar kulawa wanda kuma jamiar ce za ta dauk nauyin duk wasu kudade da za a kashe,” a cewar Akogun.