Wani tsoho mai shekara 60 da ake zargi da yin lalata da yarinya ‘yar shekara 10 bayan ya bata Naira dari 6 ya shiga komar ‘yan sanda.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ogun DSP Abimbola Oyeyemi, ya shaidawa Aminiya cewa, iyayen yarinyar ne suka shigar da qara a ofishin rundunar da ke Arebge bayan da suka lura yarinyar ta sauya dabi’unta ko da suka tambaye ta sai ta fada masu tsohon ya bata Naira dari 6 yayi lalata da ita kana wanann shi ne karo na biyu.
Yanzu haka rundunar ‘yan sandan na bincike akan tsohon mai suna Taufik Shotayo da ke zaune a unguwar Obantoko a Abeokuta, za a kuma a gurfanar da shi a kotu domin fuskantar shari’a da zarar an kammala bincike kamar yadda DSP Abimbola Oyeyemi, ya sanar.