✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama mutum 12 da ake zargin garkuwa da tagwayen Zamfara

Hukumar ‘yan sandan Najeriya ta kama mutum 12 da ake zarginsu da yin garkuwa da tagwayen Zamfara a ranar 21 ga Oktoba  2018 a kauyen…

Hukumar ‘yan sandan Najeriya ta kama mutum 12 da ake zarginsu da yin garkuwa da tagwayen Zamfara a ranar 21 ga Oktoba  2018 a kauyen Dauran Karamar Hukumar Zurmi da ke jihar Zamfara.

Kakakin hukumar ‘yan sandan Najeriya DCP Jimoh Moshood ne bayyana wadanda ake zargin a hedkwatar tsaro da ke Abuja, ya kuma ce an yi garkuwa da tagwayen ne Hassana Bala da Hussaina Bala lokacin da suke raba katin daurin aurensu.