Rundunar ‘yan sandan jihar Benuwe ta gano wasu gawarwakin maza biyu a kusa da titin jirgin kasa da ke gabar kogin Benuwe a cikin birnin Makurdi a yau Laraba.
Wakilinmu ya bayyana cewa, gawarwakin da ba a iya tantance su an kashe mutanen ne ta hanyar amfani da wuka sannan aka ajiye su a gefan kogin jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar DSP Catherine Anene, ya tabbatar da gano gawarwakin sannan an kai su dakin aje gawarwakin da ke babban asibitin jihar, sannan za a ci gaba da binciken gawarwakin da dalilin kisan da aikata.