✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An fara ɗebe ƙauna daga samun masu rai a girgizar ƙasar Morocco

Waɗanda suka tsira na matukar bukatar abinci da magunguna da wurin kwana

Masu aikin ceto sun fara ɗebe ƙauna ga yiwuwar samun mutane da da ransu a ɓaraguzan girgizar ƙasar Morocco.

Mako guda ke nan da aukuwar girgizar kasar mai ƙarfin maki 6.8, wadda ta yi ajalin mutane kimanin 3,000, wasu akalla 5,000 suka jikkata.

Girgizar kasar ita ce mafi muni cikin shekaru 60 a Morroco, inda a halin yanzu dubban mutane da suka tsallake rijiya da baya ke neman agaji a matsugunan jinƙai na wucin gadi a sassan ƙasar.

Tun bayan aukuwar girgizar ƙasar ranar Juma’a da dare ake aikin ceto a yankin Marrakech mai tsaunuka, inda kawo yanzu jami’an ceto suka ce sun daina jin ɗuriyar masu numfashi a cikin ɓaraguzai.

Duk da haka, ko a ranar Laraba sai da aka ceto wasu mutane da ransu a wasu yankuna masu tsauni da girgizar kasar ta shafa.

Wani jami’in agaji ya bayyana cewa yanayin hanyar shiga wurin ya zame musu kalubale, amma akan samu mutane da ransu.

A yayin da gwamnatin ƙasar ke ci gaba da jagorantar aikin ceto da kuma rabon kayan tallafi ga masu bukata, waɗanda suka jikkata na da matuƙar buƙatar magunguna.

Wadanda suke a matsugunan wucin gadi da gwamnatin ta samar kuma suna matukar bukatar abinci da tantuna.