Wani Bafulatani ne ya sayar da shanunsa sai wani malamin tsibbu ya ji labari, ya sa aka yi sallama da shi. Bayan sun gaisa sai malamin ya ce masa: “Da ma wani abin alheri ne na zo maka da shi.” Bafulatani ya ce: “Wane irin abin alheri ne?” Sai ya ce: “Ka kawo dukkan kudin da kake da su, zan yi maka addu’a, ka zama Sarkin Kano!” Sai Bafulatani ya ce: “Kai ba zai yiwu ba.” Sai malamin ya ce: “Allah fa za a roka!” Sai Bafulatani ya ce: “Kai, amma dai za a takura wa Allah!”
Daga Farfesa A. A. Garba Bata, 07062767748
Amma dai za a takura wa Allah!
Wani Bafulatani ne ya sayar da shanunsa sai wani malamin tsibbu ya ji labari, ya sa aka yi sallama da shi. Bayan sun gaisa sai…