✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ambaliyar Mokwa: Gwamnonin Arewa sun nemi daukin gaggawa

Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta ce ibtila'in ambaliyar da ta faru a Mokwa, Jihar Neja na bukatar a ɗauki matakan gaggawa don tallafi da hana sake…

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa ta bayyana ambaliyar ruwa mai tsanani da ta faru a Mokwa, Jihar Neja, a matsayin babbar ibtila’i, yana mai kira da a ɗauki matakan gaggawa don tallafi da hana sake faruwar hakan.

Shugaban Kungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana haka a yayin mika ta’aziyyarsa ga gwamnati da al’ummar Jihar Neja kan ambaliyar da ta faru a ranar Laraba, 28 ga Mayu, 2025, sakamakon ruwan sama mai kamar da bakin ƙwarya da ya yi sanadin rasa rayuka, bacewar mutane, da lalacewar gidaje, gonaki, da kayan more rayuwa.

Ya yaba da agajin gaggawa daga Gwamnatin Jihar Neja karkashin jagorancin Gwamna Mohammed Umaru Bago da kuma kokarin hukumomin agaji wajen aikin ceto da tallafa wa wadanda abin ya shafa.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi kira da a hada kai don kawo ɗauki cikin gaggawa da kuma samar da mafita mai ɗorewa, yana mai cewa: “Wannan bala’i ya nuna bukatar daukar matakan da za su hana sake afkuwar irin wannan annoba.”

Ya kuma tabbatar da goyon bayan gwamnatinsa wajen tallafa wa waɗanda abin ya shafa tare da fatan a samu zaman lafiya mai ɗorewa a yankin.