✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ambaliya ta lalata gidaje sama da 60 a Nasarawa

Ambaliyar ta auku ne a Kananan Hukumomin Jihar biyu

Akalla gidaje 60 da kayayyaki na miliyoyin Nairori suka salwanta sakamakon wata ambaliya da ta mamaye Ƙananan Hukumomin Jihar Nasarawa guda biyu.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar, Zachary Allumaga, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Lafiya, babban birnin Jihar ranar Asabar.

Ya ce an samu ambaliyar ce a Kananan Hukumomin Lafiya da Toto a watan Agusta, kuma ta raba mutane da dama da muhallansu sannan dukiyoyi suka salwanta.

A cewar shugaban, a Lafiya, an samu ambaliyar ce a unguwar da galibi daliban Jami’ar Tarayya da ke Lafiya ne suke zama a cikinta.

Zachary ya ce ta lalata kwamfutoci da katifu da littattafai da kayan abinci da sauran kayayyaki.

A Karamar Hukumar Toto kuwa, ya ce ambaliyar ta lalata sama da gidaje 60.

Ya ce ambaliyar ta Toto ta samu ne sakamakon zaizayar kasa.

Shugaban ya ce tuni hukumar ta fata shirye-shiryen raba kayan tallafi ga mutanen da ambaliyar ta shafa.