✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Akshay Kumar ya baje kolinsa a Dubai

Tauraron fim din Indiya, Akshay Kumar ya baje kolin fasaharsa a Dubai. Kamar yadda majiyarmu ta tabbatar, jarumin ba kawai ya tallata fasaharsa ne a…

A hagu, Akshay Kumar ne tare da Sheikh Muhammad bin Maktoum, lokacin da ya kai masa ziyara gidansa a DubaiTauraron fim din Indiya, Akshay Kumar ya baje kolin fasaharsa a Dubai. Kamar yadda majiyarmu ta tabbatar, jarumin ba kawai ya tallata fasaharsa ne a kasar ta Larabawa ba, akwai yunkurin da yake na ganin cewa ya mallaki gida na kashin kansa a kasar, kamar yadda takwarorinsa irinsu Shah Rukh Khan da Shilpa Shetty da kuma iyalan gidan Amitabh Bachchan suka yi.
dan wasan ya tabbatar da haka ne ga ’yan jarida, a yayin da ya kai ziyara kasar a farkon makon nan, a lokacin da ya kaddamar da tawagar wasan kwaikwayonsa mai taken ‘Once Upon a Time in Mumbai Dobaara.’ A cikin tawagar tasa, har da fitattun ’yan fim, Sonakshi Sinha da Imran Khan.
A yayin da Akshay ya sauka Dubai, ya samu gayyata ta musamman daga Shaikh Muhammad bin Maktoum bin Juma Al Maktoum a gidansa, inda suka tattauna kan al’amura da dama, ciki har da kudurinsa na sayen gida a Dubai.
“Dubai babban birni ne mai maraba ga baki. A duk lokacin da na kasance a cikinsa, ji nake kamar ina gidanmu.” Inji Akshay, a lokacin da yake tsokaci game da Dubai.
“Wannan ne ma dalilin da ya sanya na yanke hukuncin cewa zan mallaki gida a nan. Hasali ma, a yayin da nake kiciniyar kaddamarwa da baje kolin fasahata, a gefe daya kuma matata Tina tana can tana ta neman gidan da ya dace na saya a birnin.”
Ya kara da cewa: “Ka san akwai Indiyawa da ’yan Pakistan da yawa a nan Dubai. Yanayin birnin mai ni’ima ne da dadin zama. Idan ina cikinsa, ji nake kamar a Indiya nake. A lokacin da nake da zabin zama a wata kasa ba Indiya ba, to Dubai zan zauna har tsawon rayuwata.
Akshay Kumar dai yana auren tsohuwar ’yar fim, Twinkle Khanna kuma suna da ’ya’ya biyu, Aarab da Nitara.”