✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

A karon farko Buhari ya sa takunkumi

Ya sa takunkumin COVID-19 a ziyararsa ta farko zuwa wata kasa tun bayan bullar cutar.

A karon farko an ga Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari snaye da takunkumin kariyar cutar coronavirus a bainar jama’a.

An ga Buhari sanye takunkumin ne a lokacin ziyararsa ta farko zuwa kasashen waje tun bayan bullar cutar ta coronavirus.

Karon da aka ga Shugaba Muhammadu Buhari ya sa takunkumi a bainan jama'a.
Shugaba Buhari yayin sauka a filin jirgi a Bamako, babban birnin kasar Mali.

Ya kai ziyarar ta farko ne kasar Mali inda shugabanni daga Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) ke tattaunawa domin kawo karshen rikicin siyasa da ya barke a kasar.

Buhari na gaisawa Firai Ministan Mali Boubou Cisse, bayan saukarsa a birnin Bamako.

Taron na birnin Bamako na gudana ne karkashin jagorancin Shugaban Jamhuriyar Nijar, Mahamadou Issoufou.

Shugaba Boubacar Keita na Mali, sanye da farar hula yana gaisawa da Buhari.

Rikicin siyasar ya samo asali ne daga soke zaben wasu ‘yan majalisar Mali wanda wasu kungiyoyi suka zargi Shugaba Keita ta hannu a ciki.

Mahalarta taron na birnin Bamako da ya gudana a ranar Alhamis 23 ga Yuli, 2020

A farkon makon nan ne Buhari ya saurari rahoton rikicin daga Jakada Musamman, tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan a Abuja.

Dakarun Mali na faretin tarbar Buhari a kasarsu.