Saura kwana biyu kacal a gudanar da zaben Gwamnan jihar Bayelsa, wata babbar kotun tarayya ta Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa. Ta soke takarar dan takarar Gwamna karkashin jam’iyyar APC a jihar.
Kotun ta yanke wannan hukunci ne a safiyar yau Alhamis.
Wannan na nufin jam’iyyar APC mai mulkin kasar ba ta da dan takarar gwamna a zaben jihar da za a yi ranar Asabar.
Mai shari’a Jane Inyang ya ce David Lyon bai bi dokokin tsarin mulki ba wajen zaben fitar da gwani na jam’iyyar da aka yi ba.