✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yau za a yi jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya

A yau Juma’a ne ake sa ran za a gudanar da jadawalin Gasar Cin Kofin duniya da zai gudana a Rasha a badi idan Allah…

A yau Juma’a ne ake sa ran za a gudanar da jadawalin Gasar Cin Kofin duniya da zai gudana a Rasha a badi idan Allah Ya kaimu.

kasashe 32 ne suka haye gasar inda za a kasafta su rukuni-rukuni  takwas inda kowane rukuni zai kushin kasashe hur-hudu.  kasashe biyu ne daga kowane rukuni za su haye zagaye na biyu a yayin gasar.

Ana sa ran nuna jadawalin kai tsaye a fadin duniya a kafofin watsa labarai daban-daban ciki har da na yanar gizo da na talabijin da kuma gidajen rediyo irin su BBC da sauransu.

 Za a kalli yadda jadawalin zai kaya ne da misalin karfe biyu na rana agogon Najeriya.

Idan za a tuna, kimanin makonni biyu kenan da Aminiya ta buga labarin yadda Hukumar shirya kwallon kafa ta duniya (FIFA) ta jefa Najeriya a tukunya ta takwas amma a yanzu ne za ta san takamaiman kasashen da za ta fafata da su da kuma rukunin da za a jefa ta. 

Sau hudu kenan Najeriya take halartar gasar cin kofin duniya.  Ta halarci Gasar cin kofin duniya da aka yi a shekarar 1994 da 1998 da 2002 sai kuma wanda za a yi a yanzu a Rasha wato (Rasha 2018).

kasashen da suka haye gasar daga Afirka su ne Najeriya da Masar da Maroko da Tunisiya da kuma Senegal.

Za a gudanar da gasar ce a tsakanin ranakun 14 ga watan Yuni zuwa 15 ga watan Yulin 2018.