✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan ta’adda sun harbi shugaban rundunar tsaron al’ummar Zamfara

’Yan bindiga sun harbi Janar Lawal B. Muhammad, wanda a shi ne Darakta-Janar na Rundunar Taron Al’umma ta Jihar Zamfara.

Janar Lawal B. Muhammad, Darakta-Janar na Rundunar Taron Al’umma ta Jihar Zamfara ya tsallake rijiya da baya a hannun ’yan bindiga.

’Yan ta’addan sun harbi Janar Lawal ne a yayin harin da suka kai kauyen Kucheri da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe ta jihar.

Wani jami’in hukumar ya tabbatar mana cewa, “Gaskiya ne ’yan bindiga sun karbi Darakta-Janar na Rundunar Tsaron Al’umma ta Jihar Zamfara, a kwankwasonsa, amma yana samun kulawa a Asibitin Ƙwararru na Yariman Hakura da ke Gusau,” bayan faruwar lamarin.

A yammacin ranar Asabar ne suka tare babbar hanyar Funtua-Tsafe inda suka riƙa kai wa mahara hari, ciki har da Janar Lawal Murabus.

Aminiya ta gano cewa maharan sun yi masa mummunan rauni sakamakon harbin sa da suka yi a kwankwaso a yayin harin.

’Yan ta’addan sun kuma yi abin gaba da wasu matafiya da dama a yayin harin.