Wasu ‘yan bindiga da ake zarginsu masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da wani yaro dan shekara 11 mai suna Gbenga Segun, a Unguwar Abatuwa da ke karamar hukumar Abaji babban birnin tarayya Abuja.
Wani mazaunin unguwar da ya nemi wakilinmu da ya sakaya sunansa ya ce, `yan bindigar sun yi garkuwa da yaron ne da misalin karfe 1:45 na daren ranar Asabar.
Ya ce, a lokacin da ‘yan bindigar suka shiga gidan su yaron sun yi harbi a sama sannan msuka balle kofar gidan suka yi awon gaba da yaron.