✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Ya dace ’yan kasuwan Arewa su hada kansu’

Sakataren kungiyar ’Yan kasuwar Arewa da suke zuwa Kudancin kasar nan don sayo ’yan kunne da sauran  kayayyakin kwalliya, Alhaji Bashir Uba Hassan ya bayyana…

Sakataren kungiyar ’Yan kasuwar Arewa da suke zuwa Kudancin kasar nan don sayo ’yan kunne da sauran  kayayyakin kwalliya, Alhaji Bashir Uba Hassan ya bayyana cewa sun kafa kungiyarsu ne don yin magana da murya daya.
Alhaji Bashir ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da wakilinmu.
Ya ce domin a duk lokacin da ’yan uwanmu ’yan kasuwa na Kudancin kasar nan suka kira ’yan kasuwansu kan wani abu sakamakon yadda suke tafiya da murya daya  nan take suke amsa kira.
“Amma mu a nan Arewa a baya abin ba haka yake ba, idan muka yi kokarin mu hada kan ’yan kasuwarmu sai ka ga wasu sun fandare. Amma yanzu sakamakon kafa wannan kungiya mun fara samun hadin kai, domin a lokacin da muka kira yajin aiki na kauracewa zuwa Kudancin kasar nan, kwanakin baya nan take ’yan kasuwarmu  suka ba da hadin kai. Don haka mun fara samun narasa kan wannan kungiya da muka kafa,” inji shi.
A karshe sakataren ya yi bayanin cewa babban burin wannan kungiya  shi ne ta  tallafawa ’yan kasuwar Arewa ta kowace fanni.