✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tarihin Sa’adu Zungur: Ɗan siyasar farko a Arewacin Najeriya

Shi ne ɗan Arewa na farko da Turawan Mulkin Mallaka suka tura shi makarantar gaba da sakandare a Kudancin Najeriya

Malam Sa’adu Zungur ya shahara ne a Arewacin Najeriya sanadiyyar waƙoƙin da ya wallafa.

Amma ko kun san shi ne ɗan Arewa na farko da Turawan Mulkin Mallaka suka tura shi makarantar gaba da sakandare a Kudancin Najeriya?

Ko kun san shi ne ya fara kafa ƙungiyar siyasa a Arewacin Najeriya?

Ko kun san shi ne ya fara shirya zanga-zangar ƙin amincewa da manufar gwamnati a Arewacin Najeriya?

Ko kun san shi ne ɗan Arewa na farko da ya riƙe muƙami a jam’iyyar siyasa ta ƙasa?

Ko kun san shi ne ya fara kai ƙarar Bature kotu kuma ya yi nasara a kansa a Arewacin Najeriya?

Wannan jajirtaccen ɗan gwagwarmayar, ya rayu ne tsawon shekaru 43 a duniya kuma ya rasu ana saura shekaru biyu Najeriya ta samu ƴancin kai.