✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun fatattaki ’yan bindiga sun ceto mutum 4 a Taraba

Maharan sun tsere bayan shan ruwan wuta daga dakarun sojin.

Dakarun Sojin Najeriya tare da hadin gwiwar ’yan sanda sun lalata maboyar ’yan bindiga tare da ceto wasu mutum hudu a Karamar Hukumar Yorro a Jihar Taraba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktan hulda da jama’a na rundunar, Laftanar Olabodunde Oni, ya fitar a ranar Lahadi.

Ya bayyana cewa sun tarwatsa maboyar ’yan bindigar da suka addabi yankin Yorro da kewaye.

Ya ce sojojin sun yi arangama da ’yan bindiga a tsaunin Gampu da yankin Ban Yorro, inda suka yi wa ’yan ta’addan ruwan wuta.

“Har yanzu ana ci gaba da gudanar da aikin ceto wadanda aka sace a yankin tare da hada su da iyalansu.

“Rundunar soji ta jadadda aniyar tabbatar da tsaron lafiyar ’yan kasa da kuma tarwatsa masu aikata laifuka a jihar nan.

“An yi kira ga jama’a da su bai wa sojoji goyon baya ta hanyar bayar da sahihan bayanai don taimakawa wajen inganta tsaro.”