Shugaban Majalisar Dokokin jihar Kaduna Alhaji Aminu Shagali, ya yi murabus daga mukaminsa.
Alhaji Aminu, ya mika takardar murabu dinsa a ranar Talata lokacin da wasu ‘yan majalisar dokokin jihar ke yunkurin tsige shi daga kujerarsa.
Shugaban Kwamitin Yada Labarai na majalisar Tanimu Musa, ne sanar da takardar yin murabus da Alhaji Aminu Shagali, ya yi kuma ya ce tsohon Shugaban Majalisar zai ci gaba da aiyukansa a matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar.
Cikakken rahoton na nan tafe.