✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NUT ta bukaci gwamnoni su biya malamai basussukan da suke bi

“A wasu jihohin, malaman firamare na bin gwamnatin jihar bashin albashi na wata 18," in ji Ike-Ene.

Kungiyar Malamai ta Najeriya (NUT) ta yi kira ga gwamnonin jihohin da malaman makaranta ke bi bashi da su yi amfani da dan lokacin da ya rage musu a kan karagar mulkin su biyan hakkokin.

Sakatare-Janar na kungiyar, Dokta Mike Ike-En ne ya yi wannan kira ranar Talata a Abuja albarkacin zagayowar Ranar Malamai ta Duniya wadda za a yi ranar Laraba.

A cewar Ike-Ene, akwai gwamnoni da dama da ba su kammala biyan bashin albashin da malaman firamare da na sakandare ke bi a jihohinsu ba.

Don haka ya ce akwai bukatar gwamnonin da lamarin ya shafa su yi kokarin biyan malaman hakkokinsu a tsakanin ‘yan watannin da suka rage musu a kan mulki.

“Yawancin malaman sun koka kan rashin biyan su albashi a kan kari duk da tsadar rayuwar da ake fama da ita.

“A wasu jihohin, malaman firamare na bin gwamnatin jihar bashin albashi na watanni hudu zuwa 18,” in ji Ike-Ene.

Ranar 5 ga watan Oktoba ta kowace shekara Majalisar Dinkin Duniya ta ware don gudanar da bikin Ranar Malamai ta Duniya da zummar yabawa da kuma karfafa wa malaman makaranta gwiwa a fadin duniya.