✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NDLEA za ta sanya kyamara a jikin jami’anta

Hukumar yaki da ta'ammali da miyagun kwayoyi (NDLEA) za ta fara sanya kyamarori a jikin jami’anta domin inganta aikinsu.

Hukumar yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi (NDLEA) za ta fara sanya kyamarori a jikin jami’anta domin inganta aikinsu.

Shugaban hukumar, Mohamed Buba Marwa, ya bayyana haka ne a wani taro a Abuja inda aka yi wa wasu jami’ai karin girma a ranar Laraba.

Marwa ya ce, “Za mu sa kyamarori a jikin jami’anmu a lokacin gudanar da muhimman ayyuka don tabbatar da amincinsu da kuma ingancin ayyukan.”

Don kara inganta aikin hukumar, Marwa ya bayyana cewa NDLEA na kafa rassa biyar a Legas da Abuja.

Hukumar ta kara wa jami’anta 5,042 girma, ciki har da manyan hafsoshi biyu zuwa mukamin mataimakin kwamanda-janar.

Marwa ya ce karin girma ya biyo bayan tsauraran gwaje-gwaje da aka yi wa jami’an, yana mai bayar da tabbacin inganta yanayin aikin jami’an hukumar.