Tsohon shugaban Najeriya Cif Olusegun Obasanjo ya ce mulkin Buhari ya yi kama da na Janar Sani Abacha saboda yadda shugaba Buhari ke son ya lashe zaben 2019 don dawo mulkin kasar karo na biyu.
Obasanjo ya zargi hukumar zaben Najeriya mai zaman kanta INEC da cewa, ta shirya yin magudi a zaben 2019.