Wani saurayi ne mai son girma da yawa, shi da kannensa uku suna zaune suna cin abinci, sai ya ce wa karaminsu mai suna Adamu: “Adamu, je ka debo mani ruwa.” Shi kuma sai ya ce: “Yaya ni gaskiya abinci nake ci.” Sai wan Adamu ya ce: “Yaya, ka san Adamu ba shi da kunya, kawai ka je da kanka ka debo.” Shi kuma mai bi wa wan Adadu sai ya ce: “Yauwa, yaya idan ka sha, ka taho mani da shi.”
Daga Azzubair M. Fagge Kano, 08034412272
Masu kyuya
Wani saurayi ne mai son girma da yawa, shi da kannensa uku suna zaune suna cin abinci, sai ya ce wa karaminsu mai suna Adamu:…