✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Makelele ya zama kocin kulob din Bastia

Tsohon dan kwallon tsakiya a kulob din Chelsea Claude Makelele ya zama kocin kulob din Bastia da ke buga wasa a gasar rukunin Ligue 1…

Tsohon dan kwallon tsakiya a kulob din Chelsea Claude Makelele ya zama kocin kulob din Bastia da ke buga wasa a gasar rukunin Ligue 1 na kasar Faransa
dan kimanin shekara 41, a da shi ne mataimakin Kocin PSG, Laurent Blanc da ke Faransa.
Tuni mahukunta kulob din na Bastia suka sanar da daukar Makelele a matsayin kocinsu a kafar sadarwarsu..
“A ranar Litinin muke sa ran kocin zai sanya hannu a yarjejeniyar da muka kulla da shi sannan a washegari za mu gabatar da shi ga duniya”, kamar yadda sanarwar da kulob din ta fitar a ranar Asabar da ta wuce ta nuna.
Makele dai ya taba yi wa kulob da dama wasa da suka hada da Celta bigo da Real Madrid a Sifen da Chelsea a Ingila da kuma kulob din PSG na Faransa.