✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Romelo Lukaku ya sake komawa Chelsea

Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta sanya sayen Romelu Lukaku daga Inter Millan a kan Fam miliyan 97.5. A ranar Alhamis Lukaku, dan wasan gaban…

Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta sanya sayen Romelu Lukaku daga Inter Millan a kan Fam miliyan 97.5.

A ranar Alhamis Lukaku, dan wasan gaban kasar Belgium ya sanya hannu a takardar kwantaragin kan Yuro miliyan €115. Shi kuma zai rika samun Yuro miliyan 12 bayan haraji a karshen kowace kakar wasanni, baya ga kudaden tallace-tallace.

Bayan rattaba hannun, Chealsea ta ruwaito Lukaku yana cewa: “Ina farin cikin sake dawowa wanna kulob mai matukar ban sha’awa. Na goyi bayan Chelsea a lokacin da nake dan karam.

“Yadda kungiyar ke tafiya ya yi daidai da burine kuma bayan lashe gasar Serie A. Wannan damar ta zo a daidai, kuma za mu sanu babbar nasara a tare.”

Lukaku ya bar Chelsea ne a Gasar cin Kofin UEFA na 2013, a wasan da ya barar da bugun fenariti a karawarsu da Bayern Munich.