✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kwastam ba zata iya rufe daukacin iyakokin kasa ba- Hamid Ali

Shugaban Hukumar Kwastam Kanal Hamid Ali (mai murabus) ya bayyana cewa, hukumar ba zata iya rufe ko ina a iyakokin kan tudu na kasar nan…

Shugaban Hukumar Kwastam Kanal Hamid Ali (mai murabus) ya bayyana cewa, hukumar ba zata iya rufe ko ina a iyakokin kan tudu na kasar nan ba.

Kanal Hamid Ali, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da wakilin Aminiya. Jim kadan bayan da ya baje wa manema labarai tarin kudi Dalar Amurka miliyan 8 da dubu dari 6 da jami’an hukumar suka kama a tashar jiragen sama na Murtala Muhammad da ke Lagos, ya ce iyakokin kasar nan na kan tudu sun yi fadi da girman da ba ko ina ne jami’an hukumar zasu iya toshewa ba.

Hamid Ali shugaban Hukumar Kwastam

“Ka ga kamar yadda na nuna maku man girki na Kwanturola da shinkafa da daskararrun kaji da jami’anmu suka kama inda an rufe bodar duk, baza ku ga wannan ba, abin da nake so jama’a su gane boda ba kofa ce, nace da zaka sanya sakata ka rufe ta rufe ba, dan haka jami’an mu ba zasu iya toshe ko ina ba, dan haka dole ne mu nemi hadin kai da jama’a, dole ne mu nemi bayanan sirri, bayanan da mutane suke bamu da su muke amfani, amma muddin jama’a basa bamu goyon baya ba zamu cimma manufarmu ba.”

Shugaban na Kwastam, ya ce kudin da jami’ansu suka kama kwatankwacin Naira biliyan 2.8, ya sabawa ka’idar fita dasu, domin duk kudin da ya kai dala Amurka dubu 10, dole a sanar da hukuma in za a fitar ko a shigo da su kasar nan.