Shugaban hukumar, Isma’ila Na’abba Afakalla, ya shaida wa wakilin BBC cewa, "A shirye muke mu soma tace fina-finan da za ta rika fitowa a ciki da kuma wadanda take daukar nauyinsu".
Afakalla ya kara da cewa sun dauki wannan mataki ne bisa la’akari da gafarar da jarumar ta nemi a yi mata kwanakin baya.
A cewarsa, "Wannan baiwar Allah ta zo ofishina a shekarar da ta wuce inda ta nemi gafara kan abubuwan da ta yi a baya; na gaya mata ta je ta nemi gafarar Gwamna da Sarkin Kano kuma ta fito a gidan rediyo ta nemi afuwarsu da ta al’umar da take ciki.
"Don haka a matsayinmu na ‘yan-Adam wadanda kullum muke cikin kuskure, so muke a ja mutum a jiki kada ya fandare, shi ya sa muka yafe mata. Duk lokacin da mutum ya yi laifi ba a rufe masa hanyar tuba. Kuma ko yanzu ta kawo fim za mu tace shi", in ji shi.