Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bukaci gwamnonin jihohi su tabbatar sun biya ma’aikata hakkokin da suke binsu kafin bikin Kirsimeti.
Shugaban ya bayar da wannan umarnin ne a lokacin da yake zantawa da gwamnoni a fadar shugaban kasar a Abuja, kamar yadda Premiun Times ta ruwaito.