Bayan sauraran karar da aka yi yau a gaban Kotun Kolin Najeriya, wanda dan takarar shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP da jam’iyyarsa suka shigar a gaban Kotun Kolin domin kalubalantar nasarar shugaba Buhari a zaben ranar 23 Fabrairu 2019, kotun ta yi watsi da karar zaben.
Babban Alkalin Alkalan Najeriya Ibrahim Tanko, wanda yake jagorantar sauran Alkalan, ya ce wadanda suka daukaka karar ba su da ‘yancin yin hakan. Don haka kotun tayi watsi da karar da aka shigar.
Cikakken rahoton na nan tafe.