✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jihohin da ke sahun gaba wajen lashe lambobin yabo

Zuwa jiya Alhamis, jadawalin da Hukumar Shirya Gasar Wasanni ta Kasa karo na 19 a Abuja ta fitar ya nuna Jihar Delta ce ta farko…

Zuwa jiya Alhamis, jadawalin da Hukumar Shirya Gasar Wasanni ta Kasa karo na 19 a Abuja ta fitar ya nuna Jihar Delta ce ta farko bayan ta samu lambobin yabo 32 da suka hada da lambobin zinare 20 Da azurfa 4 da tagulla 8. Sai Jihar Ribas take ta biyu da lambobin yabo 23 da suka hada da zinare 5 da azurfa 7 da tagulla 11.

Sai Jihar Kano da ke matsayi na uku inda ta hada lambobin yabo 14 da suka hada da zinare 5 da azurfa shida da kuma tagulla uku.

Sai Edo ta hudu mai lambobin yabo 14 da suka hada da zinare 4, azurfa 4 da tagulla 6.

Sai Jihar Legas ta biyar da  lambobin yabo 12 da suka hada da zinare 4 da azurfa biyu da kuma tagulla 12.

Sai Abuja ta 6 da lambobin zinare 3 da azurfa biyu da tagulla biyu.

Sai Jihar Bayelsa ta 7 da ta hada lambobin yabo 22 da suka hada da zinare 2, azurfa 14 da tagulla 6.

Sai Jihar Ondo ta 8 da ta samu lambobin zinare 2 kacal, ba ta samu azurfa da tagulla ba. Sai Jihar Oyo ta 9 da lambar zinare 1 da azurfa 5 da tagulla 6.

Ya zuwa jiya Alhamis kimanin jihohi 15 ne ba su samu lambar yabo ko daya ba.