Wani mutum ne yana zaune da matarsa mai suna Hamida a gida, kullum idan ta yi masa laifi sai ya rika cewa zai sake ta, sai wata rana da ya gaya mata cewa zai sake ta sai ta ce masa: “Maigida kana saki na shi ke nan sai in je in auri limamin garin nan.” Da jin haka sai maigidan ya zaro ido ya ce: “To da ma ashe liman son ki yake, shi ya sa idan yana Sallah yake cewa ‘sami Allahu liman Hamida?”
Daga Rabilu Abubakar Gombe, 08036597674
Jahilci
Wani mutum ne yana zaune da matarsa mai suna Hamida a gida, kullum idan ta yi masa laifi sai ya rika cewa zai sake ta,…