✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Iran ta lashi takobin daukar fansa kan tagwayen hare-haren Kerman

Khamenei, ya lashi takobin daukar fansa mai tsanani kan harin da kasarsa ke zargin Amurka da Isra'ila sun kashe mata mutane 84

Jagoran addinin Iran, Ayatullah Ali Khamenei, ya yi alkwarin daukar fansa mai tsanani kan tagwayen hare-haren da suka kashe mutane 84 a kasar.

A ranar Alhamis ministan harkokin cikin gidan Iran, Ahmad Vahidia, ya rage adadin wadanda suka rasu a harin zuwa 84. Da farko hukumomin sun ce adadin ya kai 103.

Shguaban hukumar agajin gaggawar Iran, Jafar Miadfar, ya ce da farko an kirga wasu gawarwaki sama da sau daya, saboda tarwatsewar da suka yi, kafin daga baya a gano hakan.

Miadfar ya ce wadansu mutum 284 sun samu raunuka, inda 195 daga cikinsu ke wance a asibiti a sakamakon harin na Kudancin birnin Kerman.

Khamenei ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da Khamenei ya fitar bayan harin a ranar Labara.

Jagoran addinin ya ce “Muggan makiyan al’ummar Iran sun sake haddasa wani bala’i tare da kisan gilla ga al’ummar Kerman.”

“Da  yardar Allah za mu mayar da martani kan wannan bala’in da aka jefa al’ummarmu .”

Babban mai ba wa shugaban kasar Iran shawara, Mohammad Jamshidi ya zargi Isra’ila da Amurka da hannu a tagwayen hare-haren da suka kashe akalla mutane a Kudancin kasar.“Anna gwamnatin Amurka ta ce ita da Isra’ila ba su da hannu harin na yankin Kerman, Iran. Amma da gaske suke?,” in ji shi a shafinsa na X.

“Kada ku rudi kanku, alhakin wannan harin yana kan gwamnatocin Amurka da na Sahayoniya, masu amfani da ta’addanci.