Shugaban Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC Farfesa Mahmud Yakubu, ne ya sanar da hakan ranar Alhamis a wani taron manema labarai.
Farfesa Mahmud, ya ce jam’iyyu 16 ne kawai suka cika ka’idojin da tsarin mulkin Najeriya na 1991 (wanada aka yi wa kwaskwarima) ya tanadar.
Manya daga cikin jam’iyyun da aka soke sun hada da: NCP, wadda Gani Fawehinmi ya kafa; PCP, wadda ta zo ta biyu a zaben shugaban kasa na 2019; KOWA da kuma FDP, wadda Rabaran Chris Okotie, ya rika yi wa takarar shugaban kasa tun sanda aka kafa ta a 2006.