Rahotanni na bayyana cewa, mayakan Boko Haram sun kai hari garin Ngamgam wanda yake da nisan kilomita 50 a Gabashin garin Damasak da ke Karamar Hukumar Mobbar a jihar Borno, inda suka kashe manoma 20 a cikin gonakinsu.
Wannan harin ya sanya jama’ar garin Damasak cikin fargaba da tsoro.
Cikakken rahoton na nan tafe.