✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hajjin bana: Za a mayar wa alhazan Sokoto kudadensu

Gwamnatin Jihar Sokoto ta umarci a mayar wa maniyyata aikin Hajjin 2020 kudaden kujeru da suka biya bayan kasar Saudiyya ta soke aikin saboda bullar…

Gwamnatin Jihar Sokoto ta umarci a mayar wa maniyyata aikin Hajjin 2020 kudaden kujeru da suka biya bayan kasar Saudiyya ta soke aikin saboda bullar cutar coronavirus.

Hukumar alhazan jihar, bayan samun umarnin daga Gwamna Aminu Tambuwal, ta ce ta fara shirin mayar wa maniyyatan kudadensu nan ba da jumawa ba.

Kakakin hukumar, Shehu Muhammad Dange ya ce, “Mun umarci kananan hukumomi su tattara bayanan alhazansu domin a fara biyan su saboda kada a samu matsala”.

Kakakin ya ce za a mayar da kudaden bisa tsarin hukumar alhazai ta kasa (NAHCON), “ko da yake wasu za su so a ci gaba da ajiye kudadensu har zuwa lokacin aikin Hajjin 2021.

Ya shawarci maniyyatan da su dauki rashin samun halartar ibadar ta bana a matsayin kaddara.

Saudiyya ta dakatar da halartar aikin Hajjin 2020 ga dukkan mutanen da ba sa cikin kasar da masu shekaru fiye da 55 a yunkurinta na hana yaduwar cutar coronavirus.
Ta kuma takaita adadin alhazan zuwa kimanin mutum 10,000 tare da wajabta musu bin matakan kariya, kafin, a lokacin da kuma bayan aikin Hajjin.