✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Sakkwato za ta kashe N6.7bn wajen ciyarwar Azumi

Kowanne mutum zai samu buhun shinkafa, da na gero da kuma N5,000.

Gwamnatin Sakkwato ta ce za ta kashe Naira biliyan 6.7 domin ciyar da marayu da talakawa a watan Azumi na Ramadan.

A cewar gwamnatin, ciyarwar ta haɗa da rabon hatsi da kuma dafaffen abinci, wanda za a raba a cibiyoyin rabon abinci da ke faɗin jihar.

Gwamna Ahmed Aliyu ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da rabon hatsin ga marayu da marasa ƙarfi 18,400 a faɗin jihar, inda ya ce kowannensu zai samu buhun shinkafa, da na gero da kuma N5,000.

A nasa bangaren Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya gode wa Gwamnan bisa ƙoƙarinsa na ɗabbaka wannan shirin, tare da tabbatar masa da goyon bayansa wajen inganta rayuwar al’umma.