✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnati ta rufe makarantu bayan cutar Diphtheria ta kashe dalibai 5 a Bauchi

Gwamnatin ta ce duk makarantar da aka samu cutar a nan gaba, za a rufe ta

Dalibai biyar sun mutu sanadiyyar wata cuta da ake zargin ta Diphtheria a Karamar Hukumar Jama’are da ke Jihar Bauchi.

Shugaban Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Jihar, Dokta Rilwanu Mohammed ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Bauchi ranar Laraba.

Ya kuma ce an dauki samfurin mutum 28 a Karamar Hukumar, inda biyu daga ciki aka tabbatar da sun kamu da ita, inda ya ce za su tashi tsaye wajen dakile yaduwarta.

Shugaban ya bayyana bullar cutar a matsayin abin damuwa, kuma yanzu haka za a ci gaba da bincike domin tabbatar da ko cutar ce ta kashe su.

Ya kuma ce za a bayar da allurar rigakafi domin kare ci gaba da yaduwarta.

“Za mu fara yi wa yaranmu rigakafin tun suna mako shida a duniya, kuma babban abin dadin shi ne allurar kyauta ce.

Dokta Rilwanu ya kuma ce tuni gwamnati ta rufe dukkan makarantun da aka samu rahoton bullar cutar a yankin domin takaita ci gaba da yaduwarta.

Ya kuma ce duk makarantar da aka samu rahoton bullar cutar a Jihar, za a rufe ta.