A gobe Asabar idan Allah Ya kaimu za a yi wasa mai zafi a tsakanin kulob din Arsenal da na Liberpool a gasar firimiyar Ingila.
Wasan zai gudana ne da misalin karfe 5:30 na yamma agogon Najeriya a filin wasan Arsenal da ake kira Emirate.
Kawo yanzu kulob din Liberpool ne yake matsayi na biyu a teburin gasar da maki 26 a wasanni 10 yayin da Arsenal yake matsayi na 4 da maki 22 a wasanni 10.
Kenan, wasan na gobe zai yi matukar zafi, don dukkan kungiyoyin biyu suna neman nasara ne don ganin an dama da su a kokarin lashe gasar ta bana.
Ana sa ran gidajen kallon kwallon kafa za su cika makil da masoya kwallon kafa don ganin yadda wasan zai kaya.
Fatar mu dai a yi kallon wasa lafiya, kuma a tashi lafiya.