Bayan zaben fidda gwani da aka yi na nemar tikitin takarar zaben shugaban kasar Najeriyar a 2019 an tsaida tsohuwar Ministar Ilimi kuma shugabar ayarin gidauniya ‘Bring Back Our Girls’ Oby Ezekwesili a jam’iyyar ACPN.
Jam’iyyun ‘New Nigeria Peoples Party (NNPP), Accord (A), Allied Congress Party of Nigeria (ACPN), Zenith Labour Party (ZLP), Peoples Coalition Party (PCP) da Advanced Nigeria Democratic Party (ANDP)’ sun hada kai wajen fitar da ‘yar takarar da zata wakilce su a zaben shugabar Najeriya.
Jam’iyyun sun yanke shawarar ne jiya a Abuja don cika wa’adin hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC ta bayar.