✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dubun mai shekara 70 da ke yi wa ’yan bindiga safarar kwayoyi ta cika

Ya ce an kama shi ne a garin Jebba na jihar Neja ranar Alhamis da kulli 10 na miyagun kwayoyin.

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta cafke wani tsoho mai kimanin shekaru 70 a duniya bisa zargin yin safarar miyagun kwayoyi ga ’yan ta’addan Boko Haram da kuma ’yan bindiga a jihar Neja.

Kakakin hukumar, Mista Femi Babafemi wanda ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Asabar a Abuja ya kuma ce wanda ake zargin dan asalin garin Dallawa ne a jihar Agadez ta Jamhuriyar Nijar.

Ya ce an kama shi ne a garin Jebba na jihar Neja ranar Alhamis da kulli 10 na miyagun kwayoyin.

Kakakin ya ce asali mutumin ya kawo fatu da kiraga ne daga Nijar domin sayarwa a jihar Legas.

“Yayin da muke bincike a kansa, ya yi ikirarin cewa ya sayar da kayansa ne a kan kudi N300,000 sannan ya yi amfani da kudin wajen sayen kulli 10 na miyagun kwayoyin, kowanne a kan N25,000.

“Yana kan hanyarsa ta komawa Nijar dinne ta jihohin Arewa maso Yamma a inda yake tsayawa ya sayar da kwayoyin ga ’yan bindiga lokacin da muka kama shi a Jebba,” inji Mista Femi.

Ya kuma ambato Kwamnadan hukumar a jihar ta Neja, Aloye Isaac wanda ya ce kamun ya kara tabbatar da alakar da take tsakanin ta’ammali da miyagun kwayoyi da kuma matsalar tsaron da ta addabi Najeriya.