A yau Juma’a Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya tafi birnin Landan domin halartar taron zuba jari na Birtaniya da kasashen Afirka.
Za a gudanar da taron ranar 20 ga watan Janairun nan, wanna shi ne tafiyar Shugaba Buhari ta farko zuwa wata kasa a shekarar 2020.