✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Babi na Talatin da Hudu:

Shugaba yana sayayyar kayan bukata da kansa. dan Umar (Allah Ya yarda da su), ya ce, “Annabi (SAW) ya sayi rakumi daga wajen Umar da…

Shugaba yana sayayyar kayan bukata da kansa. dan Umar (Allah Ya yarda da su), ya ce, “Annabi (SAW) ya sayi rakumi daga wajen Umar da kansa. Kuma dan Umar ya saya da kansa. Abdurrahman dan Abubakar (Allah Ya yarda da shi) ya ce, “Wani mushiriki ya zo da tumaki sai Annabi (SAW) ya sayi akuya (tunkiya) daya gare shi, kuma ya taba sayen rakumi daga Jabir.”
548. An karbo daga Yusuf dan Isah ya ce: “Abu Mu’awiyya ya ba mu labari ya ce, A’amashi ya ba mu labari, daga Ibrahim daga Aswad daga A’isha (Allah Ya yarda da ita), ta ce: “Manzon Allah (SAW) ya sayi abinci daga wajen Bayahude bisa jinkiri da jinginar taguwarsa (sulkensa).”
Babi na Talatin da Biyar:
Sayen dabbobi da jakuna. Idan mutum ya sayi wata dabba ko taguwa alhali mai ita na kanta shin karban zai kasance ne kafin ya isa (wurin sauka)? dan Umar (Allah Ya yarda da su), ya ce: “Annabi (SAW) ya ce, wa Umar, ka sayar mini da shi, yana nufin wani rakumi mai wahalar sha’ani.”
 549. An karbo daga Muhammad dan Basshar ya ce: “Abdulwahhab ya ba mu labari ya ce, Ubaidullahi ya ba mu labari daga Wahab dan Kaisan daga Jabir dan Abdullahi (Allah Ya yarda da su), ya ce: “Na kasance tare da Annabi (SAW) a wani yaki. Sai rakumina ya rika jinkiri da ni ya gajiya. Annabi (SAW) ya zo gare ni ya ce, “Jabir ne? Na ce, “Na’am, ya ce, “Mene ne sha’aninka? Na ce, “Rakumina ya yi jinkiri da ni ya gajiya, sai na kasance a baya, sai (Annabi) ya sauka yana zungurarsa da sandarsa. Sa’an nan ya ce, “Hau, sai na hau hakika na gan shi (rakumin) ya kara sauri saboda Manzon Allah (SAW). (Annabi) ya ce, “Ka yi aure ne? Na ce, “Na’am,” ya ce, “Budurwa, ko bazawara? Na ce, “A’a, bazawara ce,” ya ce, “Me ya hana maka auren budurwa wadda za ka yi mata wasa kai ma ta yi maka wasa? Na ce, “Lallai ni, ina da ’yan uwa mata, don haka naso in auri bazawara wadda za ta hada kansu, tana yi musu kitso kuma ta lura da su. Sai (Annabi) ya ce, “Amma lallai kai za ka iso (gabato), idan ka isa gida ka hada kai da matarka za ku haifi yaro mai basira. Sa’an nan ya ce, “Shin za ka sayar da rakuminka? Na ce, “Na’am, sai ya saye shi da ukiyya daya ta zinari. Sa’an nan Annabi (SAW) ya komo a gabanina, ni kuma na komo washegari sai muka zo Masallaci na iske shi bisa kofan Masallaci ya ce, “Sai yanzu ka iso? Na ce na’am, sai ya ce “Ka bar rakuminka, shiga ka yi Sallah raka’a biyu, sai na shiga na yi Sallah ya umarci Bilal ya auna masa zinari awon ukiyya daya. Bilal ya auna mini kuma ya daidaita mini mizani. Sai na tafi har sai da na juya baya sai (Annabi) ya ce, “Kira mini Jabir, na ce, “A cikin raina yanzu mai yiwuwa zai mayar mini da rakumin nan wanda babu abin da ya kai shi bata mini rai.” Sai (Annabi) ya ce, “Karbi rakuminka kuma na bar maka kudinsa.”