✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Angola ta kora Namibia gida a Gasar AFCON

Yanzu Angola ta shiga zagayen Quarter-Finals a gasar.

Angola ta kora Namibia gida a Gasar Kofin Nahiyar Afirka ta AFCON da ke gudana a Ivory Coast bayan da ta doke ta da ci 3-0.

Dan wasan Angola, Gelson Dala ne ya zura kwallaye biyu kafin a tafi hutun rabin lokaci, kuma an dawoAgostinho Mabululu ya zura kwallo ta uku.

Wasan ya yi zafin da sai da alkalin wasa ya ba kowane bangaren jan kati – abin da ya sa dukkan su suka karasa wasan da ’yan kwallo goma-goma.

Mabululu ya kafa tarihi a Angola na zama dan wasan kasar na farko da ya taba cin kwallaye uku a gasar kofin nahiyar Afirka.

Yanzu Angola ta shiga zagayen Quarter-Finals a gasar, bayan lallasa Namibia da ta yi a filin wasa na Stade de la Paix

Wannan sakamakon wasa na nufin Angola za ta kara da wanda ya yi nasara a karawa tsakanin Najeriya da Kamaru.

Ana can dai an soma kece-raini tsakanin Najeriya da Kamaru a wasan da Redouane Jiyed na kasar Morocco ka alkalancinsa a filin wasa na Felix Houphouet-Boigny.