An sake rufe wasu karin shaguna 15 malllakar ‘yan Najeriya, wanda Kungiyar ‘yan Kasuwar Ghana ‘Ghana Union of Traders Association (GUTA)’ da ke yankin Opera Square a birnin Accra kasar Ghana ta yi.
Sake rufe shagunan ‘yan Najeriya ya zama adadin shaguna 70 kenan aka rufe wa ‘yan Najeriya da ke kasuwanci su a babban birnin kasar Ghana, hakan na neman durkusar da jarin ‘yan kasuwar.
Wasu ‘yan Najeriya da ke kasuwanci sun ce, akwai yi wuwar rufe masu shaguna a yankin Tip Toe Lane da ke Kwame Nkrumah a yau Talata.