✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An karrama Hajiyar da ta tsinci kudi a Saudiyya

Hajiyar ta mayar da dala 80,000 da ta tsinta a lokacin aikin hajjin bana.

Hajiyar da tsinci kudi dala 80,000 a Saudiyya, Aisha Nuhuche ta samu kyautar N250,000 saboda rikon gaskiya da amana.

An kuma karrama hajiyar da lambar yabo ta ‘Jakadar Rikon Gaskiya da Amana’ ta gidauniyar T.Y. Burutai.

Da yake jawabi yayin mika kyautar kudi da satifiket, shugaban gidauniyar, Ibrahim Dan Fulani ya bayyana Hajiya Aisha a matsayin mace sha yabo da ya kamata a yi koyi da ita.

Ya tunatar da ‘yan Najeriya muhimmancin yin abin da ya dace a ko da yaushe, “Bayan samun kudin Hajiya Aisha ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen mayar da kudaden ga Hukumar Alhazai ta Jihar Zamfara, inda daga nan ne aka mayar da kudaden ga hukumomin da abin ya shafa a kasar Saudiyya.”

Ya kara da cewa gidauniyar za ta ci gaba da kokarin kawo sauyi a rayuwar daidaikun mutane.

Daga nan sai ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su sanya gaskiya da rikon amana a cikin rayuwarsu ta yau da kullum, da kuma yin zabin da zai yi tasiri ga mutanen da ke tare da su.